Tuesday 10 September 2013

Duniyar Karya


A shekara ta dubu biyu da takwas (2008) a bisa dandalin sadarwa da ake kira 'facebook' ina ta rubuta tsokaci da kuma tura hotuna,inata nishadi na 

Kwatsam sai na hadu da ita,tayi ikirarin nine soyayyar rayuwar ta,ta cika ni da sakon ni 'e-mail', kuma na ji dadin duk wannan tarairaya,bisa ga dukkan alamu tana cikin kadaici kuma tana neman ta shiga soyayya. 

Ya kasance ranar alhamis sai na canza adireshin e-mail dina zuwa ga lambar waya na saboda e-mail din nawa na bani matsala,don haka yasa na barshi kafin na samu kyaransa
Ina dawowa gida bayan na sha gwagwarmaya a makaranta, sai wayar selula ta tai kara,murya mai dadi ta biyo bayan hakan ta gabatar da kanta a matsayin Firdausi Mahmud.

Ta sanar dani cewa wani kundin soyayya ne take nufi na dashi,har ta kaiga tattaro zuciya ta,ta ce tana kauna ta,a wannan halin na sha dariyata
Saboda ko kadan ban dauka da gaske take yi ba, na zaci raha ta kawo domin ta sani nishadi, amma sai ta karyata ni a bisa hakan.
Kosawa ta kama ni, har na kaiga duba shafin ta da kuma hotunan ta, abun da idanuwa na suka gani ya birge zuciyata, tunda tana cikin bukatan aboki ni kuma a shirye nike da shiga sabon lamari, kuma babu abin haufi a gareni sai muka fara ganawa akai-akai.
Ta yi ta nanata irin soyayyar da take min, cikin 'yan kwanaki kadan muka fara magana tamkar soyayyar mu ta dauko asali ne tun yarunta, har sai da ta sauya tunani na zuwa ga zaton qila mu zamto ma'auratan juna.
Na tuna kalmomin ta, ta taba gaya min cewar nine abin da tafi so kuma ba zata taba ajiye ni ba domin daukan wani abu komin dadin sa.
Mun shirya haduwa saboda tana zaune ne a abuja yayin da ni kuma a Lagos nike, da na sauka sai dan'uwan ta ya shigar dani cikin gidan su, suna da azirki sosai idanuwa na sun gaskata min da haka.
Amma a yayin da na kyalla idona akan sarauniyar tawa, sai na dimautu/dimauce, kuma gashi tausayi ba zai bari nai mata rashin adalci ba, amma kuma ta boye min wani abu da sai ayau na gane wa kaina.
Tabbas itace yarinyar da na gani a hoto, cike da kyawo amma sai dai kafa daya kawai gare ta.

****Zayyana min abin da za kayi/ ko zaki yi, idan hakan ta kasance gareka/ki a matsayin da na samu kai na aciki****
Ku ziyarci mu a: facebook.com/nishaaaddi
Twitter:@Ni_shaaaddi
Email:nishaaadi@gmail.com

No comments:

Post a Comment